Atiku Ya Rarrashi 'Yan Wasan Super Eagles

Atiku Abubakar (Instagram/ Atiku Abubakar)

Tun da aka fara gasar a farkon watan Janairu, babu kasar da ta yi nasara akan Najeriya sai Tunisia.

Tsohon mataimakin shugaba Najeriya Atiku Abubakar ya yi kira ga ‘yan wasan Super Eagles da kada su karaya duk da cewa an fitar da su a gasar cin kofin nahiyar Afirka da ake yi a Kamaru.

A ranar Lahadi Tunisia ta sallami Najeriya a gasar bayan da ta lallasa ta da ci daya mai ban-haushi a zagayen ‘yan 16.

“Kada mu taba karaya. Ina mai jinjina wa ‘yan wasa da daukacin tawagar kungiyar Najeriya bisa nasarorin da suka samu.

“Mun sha kaye a gasar AFCON 2021 a wannan mataki, amma ya kamata mu mayar da hankalinmu kan wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya a Qatar wanda za mu buga da Ghana.” Atiku ya ce.

Tun da aka fara gasar a farkon watan Janairu, babu kasar da ta yi nasara akan Najeriya sai Tunisia.

‘Yan wasan Agustine Eguavoen na Super Eagles sun doke Egypt da ci 1-0, Sudan 3-1 da Guinea-Bissau da ci 2-0 a rukunin D, nasarorin da suka ba su damar shiga zagayen na wasannin kwaf daya.