WASHINGTON, D. C. - Mai magana da yawun ‘yan sandan jihar Maryland Elena Russo ta ce a cikin sakon da ta aike ta wayar tarho cewa “ana nan ana kokarin dawo da martabar gadar”.
Gadar Baltimore da ta ruguje
Ba a samu gano mutane shida ba, kuma da ake kyautata zaton sun mutu, daga cikin ma’aikatan da ke aikin gyaran ramuka a kan gadar.
Ya ce shida daga cikin ma’aikatan kamfanin ana kyautata zaton sun mutu kuma ma’aikaci daya na kwance a asibiti.
Wani babban jami'in kamfanin Brawner Builders, kamfanin da ya dauki ma'aikatan gine-ginen Jeffrey Pritzker, ya ce ma'aikatan jirgin na aiki ne a tsakiyar gadar lokacin da hadarin ya faru.
Gadar Baltimore, Maryland
Ya ce har yanzu ba a gano gawarwakin ma’aikatan ba, amma ana kyautata zaton sun mutu idan aka yi la’akari da zurfin ruwan da kuma tsawon lokacin da aka dauka tun bayan hadarin.
Wani ma’aikacin kamfanin gine-ginen ya ce an gaya masa cewa abokan aikinsa da suka bace suna hutawa ne, wasu kuma na zaune a cikin manyan motocinsu a lokacin da wata gadar Baltimore ta ruguje da sanyin safiyar Talata bayan da wani jirgin ruwan mai dakon kwantena ya kara da gadar.
Ana ta aikin ceto a gadar Baltimore
Ma'aikacin Brawner Builders Jesus Campos ya ce ya sami labarin bala'in daga wani abokin aikinsa ne kuma nan da nan ya damu saboda abokan aikin nasa suna aiki a kan gadar.
A yanzu haka dai masu bincike sun gano rumbun bayanan jirgin kamar yadda suka shaida wa kafar labarai ta CBS.
Hakazalika, hukumar kula da harkokin sufuri ta Amurka, ta tabbatar da gano rumbun bayanan jirgin mallakar kamfanin Dali.
-AP