An Tarwatsa Yunkurin Kai Hare-Haren Kunar Bakin Wake A Najeriya

Amurka kuma ta gargadi Amurkawa da su yi hattara saboda akwai yiwuwar kai hare-hare kan wasu hotel-hotel dake Lagos a lokacin bukukuwan sallah gobe da jibi

Sojojin Najeriya sun murkushe wani yunkurin kai hare-haren bam na kunar-bakin wake da wasu mata na kungiyar Boko Haram suka yi.

Kakakin sojojin Najeriya, Kanar Sani Kukasheka Usman, ya ce sojoji sun harbe matan suka kashe su kafin su tayar da bama-baman dake jikinsu a kusa da wani sansanin ‘yan gudun hijira.

Wasu daga cikin bama-bama dake jikin maharan sun tashi bayan da aka harbe su.

Fararen hula biyu sun ji rauni a wannan lamarin da ya faru a bayan garin Monguno dake Jihar Borno a yankin arewa maso gabashin Najeriya, inda kungiyar ta Boko Haram ta yi tunga.

Sanarwar ta ce wata ‘yar kunar-bakin-wake ta tayar da nata bam din ta kashe kanta a wani wuri. Babu wanda ya ji rauni daga ta ukun.

A halin da ake ciki, Amurka ta yi gargadi yau talata game da yiwuwar kai hare-hare a kan ‘yan kasashen waje a cibiyar kasuwanci ta Najeriya, lagos a lokacin bukukuwan Sallar azumin nan.

Wata sanarwar da aka buga a shafin intanet na ofishin jakadancin Amurka a Najeriya, tace kungiyoyi masu alaka da ayyukan ta’addanci suna shirya kai hare-hare a kan hotel hotel inda baki ‘yan kasashen waje suka fi zuwa a Lagos, ciki har da wadanda ke bakin ruwa.

Gargadin bai ambaci sunan wata takamammiyar kungiya ba, amma kuma ya bukaci Amurkawa da su sanya idanu sosai kan abubuwan dake faruwa a kusa da su, su kuma rika kasa kunnuwa ga kafofin labarai na inda suke.