Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wani Hatsarin Kwale-Kwale A Mozambique Ya Kashe Mutane 8


Hadarin Kwale Kwale
Hadarin Kwale Kwale

Hukumomin gundumar Caia sun shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa, kwale-kwalen na dauke da mutane 12 galibi manoma.

Wani kwale-kwalen kamun kifi ya nutse a kogin Zambezi da ke tsakiyar kasar Mozambique, inda ya kashe mutane takwas da suka hada da yara shida.

Kifewar kwale-kwalen ta ranar Litinin a lardin Sofala na zuwa ne mako guda bayan wani hatsarin jirgin ruwa ya halaka mutane kusan 100, yawancinsu kananan yara, a tazarar kimanin kilomita 1,000 (mil 600) zuwa arewa.

Hatsarin kwale-kwale
Hatsarin kwale-kwale

Hukumomin gundumar Caia sun shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa, kwale-kwalen na dauke da mutane 12 galibi manoma.

Mutane biyu ne suka tsira da ransu, wasu biyu kuma ba a gansu ba. Yara shida na cikin wadanda suka mutu.

Hukumomi sun ce ana ci gaba da neman wadanda suka bace.

A ranar 7 ga watan Afrilu, wani jirgin ruwa dauke da kaya ya kife ya kashe mutane 98. Jirgin na dauke da iyalai da dama da suka firgita yayin da su ke kokarin tserewa barkewar cutar kwalara.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG