Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

A Kalla Mutane 40 Sun Rasa Rayukansu A Wani Hadarin Jirgin Ruwa A Jihar Taraba


Hadarin kwale-kwale a Jihar Taraba
Hadarin kwale-kwale a Jihar Taraba

A kalla mutane sama da 40 ne suka rasa rayukansu a wani hadarin kwale-kwale da ke dauke da mutane akalla 200 da ya nutse a kogin Billari a karamar hukumar Karim Lamido ta jihar Taraba. 

TARABA, NIGERIA - Yanzu haka dai ba gama sanın yawan mutanen da suka mutu ba, ciki har da mata da yara kanana da ma jarirai. Ya zuwa yanzu ana ci gaba da neman wadanda suka mutu a cikin jimlar mutane 200 da suke cikin jirgin ruwan.

Hadarin kawale-kwale a Jihar Taraba
Hadarin kawale-kwale a Jihar Taraba

Safiyanu Muhammad na daya daga cikin wadanda suka tsallake rijiya da baya a hadarin jirgin ruwan. Ya ce sun shiga wani guri ne da aka tare don kamun kifi sai jirgin na su ya kasa wucewa, sai ya koma da baya har ya bugi wani itacen da aka tare ruwan da shi, kawai sai suka nutse nan take.

Alhaji jidda Sulaiman, shugaban riko na kungiyan masu kula da zirga zirgar jiragen ruwa na jihar Taraba, ya kuma tabbatar mana da faruwar lamarin amma ya ce direban jirgin ruwa ne ya dauki fasinja da yawa shi ya sa hakan ya faru.

Hadarin kwale-kwale a Jihar Taraba
Hadarin kwale-kwale a Jihar Taraba

Wani mai suna Yusuf Ali kuwa ‘yan uwansa su 12 ne a cikin jirgin amma gawa biyu kadai aka samu zuwa yanzu kuma ana kan neman sauran.

‘Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Karim Lamido, Hon. Anas Shaibu Didango, ya ce sun samu labarin nutsewar jirgin ruwan kuma bisa ga labaran, mutane sama da 40 ne suka mutu.

Lokacin wani hadarin kwale-kwale a Jihar Taraba
Lokacin wani hadarin kwale-kwale a Jihar Taraba

Yanzu haka ana kan neman sauran gawarwakinsu daga cikin ruwan, ya kuma bukaci ‘yan uwan wadanda suka rasa ransu da su yi hakuri su dauki dangana, domin za su yi dukkannin mai yiwuwa don ganin an kawo karshen yawan hadarin jirgin ruwa a wannan yankin.

SP Usman Abdullahi, kakakin rudunar ‘yan sandan jihar Taraba, ya ce kawo yanzu dai ba a samu cikakken yawan wadanda suka mutu ba sakamakon wannan hadarin jirgin ruwa.

Saurari cikakken rahoto daga Lado Salisu Garba:

Akalla Mutane 40 Sun Rasa Rayukansu A Wani Hadarin Jirgin Ruwa A Jihar Taraba.mp3
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:52 0:00

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG