Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Trump Yana Da Kariya Da Ta Shafi Ayyukan Gudanar Da Mulki-Kotun Kolin Amurka


Wadansu Jami'an tsaro suna tsaye a bakin Kotun Kolin Amurka, Washington, July 1, 2024.
Wadansu Jami'an tsaro suna tsaye a bakin Kotun Kolin Amurka, Washington, July 1, 2024.

Kotun kolin ta yanke hukunci jiya Litinin cewa, shugabannin Amurka suna da kariya daga tuhuma kan laifukan da suka aikata lokacin da suke kan karagar mulki, kuma suna da cikakkiyar kariya daga gurfanar da su a gaban kotu a kan abinda su ka aikata yayinda su ke gudanar da aikin Shugaban kasa.

Lamarin dai ya samo asali ne daga ikirarin da tsohon shugaban kasar Donald Trump ya yi na cewa, ba a da hurumin gurfanar da shi a gaban kotu a kan kokarin da ya yi na sauya sakamakon zaben shugaban kasa na 2020 da ya nuna ya sha kaye, da ya kai ga gungun magoya bayansa da suka kutsa kai cikin Majalisar Dokokin kasar tare da kawo cikas ga tabbatar da zaben shugaba Joe Biden.

Mafi tasirin hukuncin nan da nan shi ne cewa, kusan ya ba da tabbacin cewa ba za a yanke hukunci kan tuhume-tuhumen da gwamnatin tarayya ke yi kan yunkurin kifar da zaben shugaban kasa na 2020 ba kafin zaben 2024, da Trump ke takara karkashin tutar jam’iyar Republican. Idan har ya ci zabe, zai iya sa a yi watsi da karar gaba daya.

'yan takarar shugaban kasar Amurka
'yan takarar shugaban kasar Amurka

Abin jira a gani shi ne yadda wannan hukunci zai shafi yadda shugabannin da za su gudanar da rayuwarsu a yayin da suke kan karagar mulki, sai dai masana da dama sun ce matakin na iya bude kofar wuce gona da iri.

Alkalan kotun shida masu ra'ayin mazan jiya ne da su ke da rinjaye, suka fitar da ra'ayin da babban mai shari'a John Roberts ya rubuta, a rana ta karshe ta tsawaita wa'adin, yayin da alkalai masu sassaucin ra'ayi guda uku suka yi allah-wadai da wannan matsayin.

Tsohon Shugaban kasar Amurka Donald Trump
Tsohon Shugaban kasar Amurka Donald Trump

Alkalan mafiya rinjayen dai sun kawar da yiwuwar tuhumar Trump kan wasu abubuwa da ya yi bayan zaben da suka hada da yi wa jami’in ma’aikatar shari’a barazanar kora daga aiki sai dai idan ya yi karyar cewa hukumar na binciken yiwuwar magudi a wasu jihohin da suka zabi Biden.

Sai dai sun bar yuwuwar cewa masu gabatar da kara za su iya kalubalantar kariyar a kan wadansu ayyukan da ya gudanar a matsayin Shugaban kasa, suka bar kananan kotuna su yanke wannan shawarar.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG