Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Trump Yayi Barazanan Dakatar DaTaimakon Da Amurka Ke Ba Falasdinawa


Shugaba Donald Trump yana shan hannu da Firai Ministan Isra'ila Benjamin Netanyahu
Shugaba Donald Trump yana shan hannu da Firai Ministan Isra'ila Benjamin Netanyahu

Shugaban Amurka Donald Trump ya nemi sanin ko za a sake komawa kan teburin tattaunawa tsakanin Isra’ila da Falasdinu

Trump ya fadi hakan ne yayin da yake ganawa da Firayi Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu a wurin taron kolin tattalin arziki na kasashen duniya a birnin Davos na kasar Switzerland, inda ya zargi Falasdinawa da rashin girmama Amurka, bayan da Shugaban Falasdinu Mahmoud Abbas yaki ganawa da mataimakin shugaban Amurka Mike Pence yayin da yake ziyara a yankin.

Trump yayi barazanan yanke taimakon da Amurka ke yiwa Falasdinawa.

Wani bangaren kudin taimakon ne zuwa kai tsaye a hannun hukumomin Falasdinawan, yayin kaso mai yawa ke zuwa ga kungiyoyi masu zaman kansu da kuma kungiyoyin bada agaji dake aiki a wurin.

Idan aka kwatanta da taimakon da Amurka ta baiwa Isira’ila, a shekarar 2016, na dala biliyon uku da miliyon dari na taimakon soji. Kudin taimakon zai karu a shekarar ta 2019.

Ba za’a iya sa farashi akan yanci da mutuncin wata al’umma ba. Jiya Alhamis jakadan Falaadinawa a Majalisar Dinkin Duniya Riyad Mansour ya yi wannan furucin a New York. Yace ba zasu girgiza da barzana ko tsoratarwa ko wata muguwar niya ba, kuma ya kamata duk wani mai son zaman lafiya da adalci kuma ya amince da dokokin kasa da kasa yayi Allah wadai da wannan abu.

Mansour yayi wadannan kalaman ne a wani zama da kwamitin sulhun MDD yayi a kan Gabas ta Tsakiya.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG