Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tinubu Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar Alhazai Bayan Sauke Jalal Arabi


Sabon shugaban hukumar Alhazain Najeriya, NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman (Hoto: Facebook/Isa Ade)
Sabon shugaban hukumar Alhazain Najeriya, NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman (Hoto: Facebook/Isa Ade)

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC na tuhumar Arabi kan yadda aka sarrafa naira biliyan 90 da gwamnatin tarayya ta bayar don tallafa wa aikin hajjin 2024.

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya nada Farfesa Abdullahi Saleh Usman a matsayin sabon shugaban hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON.

Nada Farfesa Usman ya biyo bayan sauke Jalal Arabi, wanda ya shugaban ya nada a bara.

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC na tuhumar Arabi kan yadda aka sarrafa naira biliyan 90 da gwamnatin tarayya ta bayar don tallafa wa aikin hajjin 2024.

Tsohon shugaban Hukumar NAHCON, Jalal Ahmed Arabi
Tsohon shugaban Hukumar NAHCON, Jalal Ahmed Arabi

Ana zargin Arabi da wasu jami'an hukumar da karkata akalar wani adadi na wadannan kudade.

Wata sanarwa da kakakin Tinubu Ajuri Ngelale ya fitar a ranar Litinin ta ce Farfesa Usman fitaccen malami ne da ya yi karatu a Jami’ar Madinah da Jami’ar Pashewar da ke Pakistan.

“Sannan ya san kan aikin hajji duba da cewa ya taba rike hukumar alhazai ta jihar Kano wacce ta fi yawan alhazai a duk fadin kasar.

“Nadin zai tabbata idan majalisar dattawa ta sahale.” In ji Ngelale.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG