Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sufeton ‘Yan Sandan Najeriya Ya Sake Watsi Da Goron Gayyatar ‘Yan Majalisa


Sufeto-Janar na 'yan sandan Najeriya, Ibrahim K. Idris
Sufeto-Janar na 'yan sandan Najeriya, Ibrahim K. Idris

A karo na uku, babban sufeton ‘yan sandan Najeriya, Ibrahim Idris ya ki amsa goron gayyatar da Majalisar Dattawa ta yi masa.

Wannan dai shine karo na uku da Majalisar Dattawan Najeriya ke gayyatar sufeton ‘yan sandan Najeriya, domin ya bayyana gaban Majalisar ya yi bayani kan kashe-kashen dake faruwa a wasu jihohin kasar.

Haka kuma ana tsammanin zai yiwa ‘yan Majalisar bayani kan zargin cin zarafin da ‘yan sanda su ka yiwa ‘dan Majilsa Dino Melaye, wanda ya shafe makonni biyu a hannunsu.

Bayan yin shiru na wajen mintina goma a zauren Majalisa ana jiran shigowar Ibrahim Idris, sai shugaban Majalisar Bukola Saraki ya sanar da cewa sufeto din bai zo ba. kuma babu wani wakilinsa da ya aika.

Yanzu haka dai ana jiran ganin wanne mataki da kundin tsarin mulkin kasa Majalisar za ta dauka domin hukunta sufeton ‘yan sandan, bisa laifin yin watsi da umarnin ta.

Facebook Forum

TASKAR VOA: Fim Da Aka Shirya Kan Leah Sharibu Ya Samu Lambar Yabo
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:26 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
TASKAR VOA: Kalubalen Da Masu Fama Da Lalurar Galhanga Ke Fuskanta
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:26 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
TASKAR VOA: Tasirin Cibiyar Kula Da Lafiyar Mata Da Yara Ta HopeXchange A Ghana
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:41 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
TASKAR VOA: Hukumomi Sun Fara Shirin Bada Gudumawar Jini A Fadin Najeriya
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:54 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG