Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Nijar Ta Dauki Matakin Hana Fitar Da Hatsi Zuwa Ketare


Wasu 'Yan Kasuwa Na Auna Shinkafa
Wasu 'Yan Kasuwa Na Auna Shinkafa

A yayinda aka fara girbe amfanin gona a yankuna da dama na jamhriyar Nijar ofishin ministan kasuwanci ya hana fitar da abincin da suka hada da shinkafa da hatsi da dawa zuwa ketare da nufin samar da wadatar cimaka akan farashi mai rangwame a kasuwannin kasar.

Ganin yadda a irin wannan lokaci na kaka wasu ‘yan kasuwar kasashen waje da ma wasu a nan cikin gida ke saye amfanin gona da arha kuma su jibge don sayarwa a gaba da tsada ya sa gwamnatin Nijar kafa dokar hana fitar da abincin da suka hada da hatsi da shinkafa da dawa.

Shugaban kungiyar ADDC WADATA mai fafutikar kare hakkin masu saye don amfani Malan Maman Nouri na cewa abin na iya tasiri wajen wadatar da jama’a da cimaka ya kuma yi sanadin saukar farashi a kasuwanni.

Sai dai hukumomin sun ce matakin bai shafi sauran kasashen kungiyar AES ba wato Mali da Burkina Faso a bisa wasu dalilai.

Galibin jama’ar Nijar musamman mazauna karkara na dogara da noman damuna don tanadin cimaka, galibi dawa da hatsi da wake yayinda a wasu yankunan a kan kwatanta noman shinkafa.

La’akari da yadda canjin yanayi ya fara shafar sha’anin damuna ya sa hukumomi da kungiyoyin ci gaban al’umma kwadaitar da ‘yan kasar fa’idar maida hankali kan ayyukan noman rani musamman a shekarun da aka fuskanci gardamar damuna.

Sararım çıkakken rahoto daga Souley Moumouni Barma:

Nijar Ta Dauki Matakin Hana Fitar Da Kayan Amfanin Gona Don Wadata Kasar
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:15 0:00

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG