Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Najeriya Ta Kwaso ‘Yan Kasarta 390 Daga Nijar


Ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Tuggar
Ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Tuggar

Hukumar Kula da 'Yan Gudun Hijira, 'Yan Ci Rani da Masu Gudun Hijira a Cikin Gida (NCFRMI) ce ta karbe su a Makarantar Horas da Ma’aikatan Shige da Fice da ke Kano a cewar rahotanni.

Gwamnatin Najeriya ta yi nasarar mayar da 'yan kasarta 390 da suka makale a birnin Yamai, Jamhuriyar Nijar zuwa gida.

Hukumar Kula da 'Yan Gudun Hijira, 'Yan Ci Rani da Masu Gudun Hijira a Cikin Gida (NCFRMI) ce ta karbe su a Makarantar Horas da Ma’aikatan Shige da Fice da ke Kano a cewar Voice of Nigeria (VON.)

Kwamishinan Hukumar NCFRMI na Tarayya, Tijjani Ahmed, wanda Mai Kula da Ofishin Kano, Hajiya Lubah Liman, ta wakilta, ya sake jaddada kudurin gwamnati na kare 'yan kasa da kuma sake hada su cikin al’umma.

Ya sanar da cewa wadanda aka dawo da su za su ci gajiyar shirye-shiryen tallafawa karkashin shirin Renewed Hope Agenda” na Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ke karawa jama’a kwarin gwiwa.

“Da isowar su, an yi wa dukkan wadanda aka dawo da su rijista tare da daukan bayanansu don samun damar shigar da su cikin shirye-shirye na ba da tallafin.” in ji Ahmed.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG