Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kotu Ta Haramta Wa Pauline Tallen Rike Mukamin Gwamnati A Nijeriya


Pauline Tallen
Pauline Tallen

Babbar Kotun Tarayya da ke birnin tarayya, Abuja ta haramta wa tsohuwar Ministar Mata da Walwalar Al’umma, Pauline Tallen sake rike wani mukamin gwamnati.

Babbar kotun tarayyar ta yanke hukumcin ne bayan sauraron karar da kungiyar NBA ta shigar a kan Pauline Tallen.

Kungiyar lauyoyin Najeriya ta maka tsohuwar Ministar a kotu saboda ta soki hukuncin da kotu ta yi a baya.

A wani hukunci da ta yanke a ranar Litinin, kotun ta yi tir da kalaman da tsohuwar ministar ta yi a shekarar da ta wuce, inda ta caccaki wani hukuncin kotun tarayya da ke Jihar Adamawa.

Zaman Kotu
Zaman Kotu

Kotun da ke zamanta a birnin Yola, babban birnin Adamawa, ta soke cancantar takarar A'ishatu Dahiru da aka fi sani da Binani ta jam'iyyar APC da ke neman kujerar gwamnan a wancan lokacin.

Sai dai Tallen ta nuna rashin gamsuwarta da hukuncin na kotun wanda ta bayyana a matsayin "musguna wa wani bangare na al'umma", yayin da ta bukaci 'yan Najeriya da su yi watsi da hukuncin.

Aisha Binani
Aisha Binani

Kotun ta ce kalaman Tallen sun saba doka, kuma akwai ganganci da takaici da kuma rashin yi wa bakinta linzami.

Saboda haka Alkali ya zartar da hukunci cewa dole ta nemi afuwa, ko kuwa ba za ta sake iya rike mukami ba.

Sai dai tsohuwar Ministar ta nuna halin ko-in-kula, lamarin da ya sa kungiyar lauyoyin ta maka ta a gaban kotu.

Duk yunkurin jin ta bakin Pauline kan hukumcin kotun ya ci tura.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG