Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

2024: Jami’an ‘Yan Sanda 140 Ne Suka Mutu A Abuja


'Yan Sanda A Jihar Zamfara
'Yan Sanda A Jihar Zamfara

Wasu daga cikin iyalan mamatan sun riga sun karbi hakkokinsu da sauran tallafi kamar yadda babban sufeton ‘yan sandan Najeriya, Kayode Egbetokun ya ba da umarni.

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce ta yi asarar jami’anta 140 da ke aiki a birnin tarayya, Abuja, a shekarar 2024 da ta gabata.

A sanarwar karshen shekarar da rundunar ‘yan sandan Abuja ta fitar game da nasarorin da ta samu tun daga watan Janairu zuwa Disemban 2024, kwamishinan ‘yan sanda, Olatunji Disu ya ce wasu daga cikin zaratan jami’ansa 140 sun mutu sakamakon arangama da ‘yan shi’a da wasu nau’ukan tarzoma da cutar hawan jini a birnin Abuja a 2024.

Ya kuma bayyana cewa wasu jami’an ‘yan sandan sun mutu a cikin baccinsu a yayin da wasu suka yanke jiki suka fadi a bakin aiki.

A cewarsa, wasu daga cikin iyalan mamatan sun riga sun karbi hakkokinsu da sauran tallafi kamar yadda babban sufeton ‘yan sandan Najeriya, Kayode Egbetokun ya bada umarni.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG