Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jamhuriyar Nijer Za Ta Fara Zagaye Na 2 Na Kamfen Din Riga Kafin Covid 19


Allurar riga kafi.
Allurar riga kafi.

Yau talata 15 ga watan Yuni ake fara zagaye na 2 na kamfen riga kafin cutar covid 19 a jamhuriyar Nijer inda za a kafa asibitocin tafi da gidanka a mashigar ma’aikatun gwamnati tashoshin shiga motocin haya da filayen jirgin sama da gidajen hakimai da masu unguwa .

Lura da yadda annobar corona ke kara tsananta a wasu kasashen waje inda aka fara samin bular wani sabon nau’in kwayar cutar ya sa hukumomin Nijer soma yunkurin tsaurara matakan riga kafi mafarin wannan kamfe da za a fara a yau talata 15 ga watan yuni kamar yadda ministan kiwon lafiyar al’uma Dr Iliassou Idi Mainassara ya bayyana a taron manema labaran da ya kira.

Tuni aka kebe wasu wuraren musamman domin gudanar da wannan aiki na tsawon mako 1 saboda haka aka bukaci al’umma ta baiwa likitoci hadin kai.

Daga lokacin gano mutun na farko da ya kamu da cutar corona a nan Nijer a watan maris na 2020 kawo jiya litinin 14 ga watan Yuni mutum 5452 aka bayyana cewa sun harbu da kwayar cutar a wannan kasa daga cikinsu 5172 suka warke yayinda a yanzu haka mutum 88 ke asibiti domin karbar magani kuma bayanan hukumomin kiwon lafiya sunce mutane 192 ne cutar ta covid 19 ta kashe a tsawon wannan lokaci saboda ake kara kiran jama’a a ci gaba da biyayya ga matakan riga kafi.

Domin karfafa zagayen farko na allurar riga kafin da aka kaddamar a ranar 28 ga watan maris din da ya gabata ne hukumomin lafiya suka shirya zagaye na 2 da ke somawa daga yau talata 15 ga watan Yuni.

Saurari cikakken rahoton a cikin sauti:

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:49 0:00

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG