Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hukumar USAID Ta Kai Ziyara Cibiyar Mata Masu Zaman Kansu a Jihar Bauchi


Hukumar USAID Ta Kuduri Aniyar Tallafawa Wasu Jihohin Nijar
Hukumar USAID Ta Kuduri Aniyar Tallafawa Wasu Jihohin Nijar

Hukumar samar da agaji kasa da kasa na kasar Amurka USAID, a Jihar Bauchi ta kai ziyara ganewa ido wata cibiyar da mata masu zaman kansu da ke samun horo kan sana’a iri dabam dabam da zai inganta rayuwar matan bayan sun kammala samun kwarewa.

BAUCHI, NIGERIA - Sai dai tun da farko hukumar ta USAID ta gudanar da taron fadakarwa kan muhimmancin ranar mata na Duniya da kuma jan hankulan hukumomi game da bukatun mata don samun cigaba.

Honorable Maryam Garba Bagel, kwamishinar ma’aikatar wutar lantarki, kimiyya da kuma fasahar a jihar Bauchi, ta yi bayani kan bukatun mata, samun ci gabansu da sauran abubuwan da suka shafesu.

Daga bisani hukumar ta USAID ta ziyarci cibiyar da aka kebe domin koya wa matan sana’a, wanda ke karkashin kulawar hukumar Hisba ta hukumar shari’a ta Jihar Bauchi.

Saurari rahoton Muhammad Abdulwahab cikin sauti:

Hukumar USAID Ta Amurka A Jihar Bauchi Ta Kai Ziyara Cibiyar Mata Masu Zaman Kansu Dake Samun Horon Sana’o’i
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:12 0:00

XS
SM
MD
LG