Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Manyan Malaman Jami'o'i Sun Gudanar Da Zanga-Zanga A Fadin Najeriya Kan Bashin Albashi


SSANU/NASU
SSANU/NASU

Mambobin Kungiyar Manyan Malaman Jami’o’in Najeriya (SSANU) da takwarorin na Ma’aiktan Da Ba Malamai Ba (NASU) sun gudanar da zanga-zanga a harabar jami’o’in dake fadin Najeriya a yau Talata domin neman a biyasu kudaden albashin da suke bi bashi.

Fusatattun ma’aikatan na dauke da kwalaye masu dauke da mabambantan sakonni a sa’ilin da suke gudanar da maci a cikin harabar jami’o’in, inda suke kira ga gwamnatin tarayya ta sakar musu albashin da ta rike musu tare da aiwatar da sauran bukatunsu.

Zanga-zangar mambobin SSANU da NASU a Ilori
Zanga-zangar mambobin SSANU da NASU a Ilori
Zanga-zangar mambobin SSANU da NASU a Owerri
Zanga-zangar mambobin SSANU da NASU a Owerri

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG