Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Dakarun Nijar Sun Kashe Mayakan ISWAP 10 A Kan Iyakar Nijar Da Najeriya


Dakarun Nijar
Dakarun Nijar

Samun wannan galaba na zuwa ne a daidai lokacin da talakawa a wasu kasashen yankin Sahel ke zargin mahukunta da gazawa a fannin samar da tsaro.

Hukumomin a Jamhuriyar Nijar sun yi ikirarin cewa dakarun kasar sun fatattaki mayakan kungiyar ISWAP lokacin da suka kai hari a sansanin sojan Chetima Wango dake jihar Diffa kusa da iyakar Nijar da Najeriya.

A wata sanarwar da aka bayar mai dauke da sa hannun ministan tsaron kasa Alkassoum Indatou, ma’aikatar tsaron Nijar ta ce wani ayarin motoci 7 dauke da mayakan kungiyar ISWAP da suka tsallako daga Najeriya ya kai hari akan sojojin dake da sansani a kauyen Chetima Wangou na yankin Diffa.

Harin a cewar sanarwar an kai shi ne da misalin karfe 7:30 na safiyar Asabar 29 ga watan Janairu, martanin da askrawan na Nijar suka mayar ya ba su damar hallaka mutun 10 daga cikin maharan tare ragargaza masu motoci uku.

A cewar hukumomin kasar, akwai wadanda suka tsira da sauransu suka gudu suka bar mota daya sakamakon wuyar da suka sha.

Samun wannan galaba na zuwa ne a daidai lokacin da talakawa a wasu kasashen yankin Sahel ke zargin mahukunta da gazawa wajen shawo kan matsalolin abin a yaba ne in ji editan jaridar la Roue de l’histoire Ibrahim Moussa magatakarda a kungiyar ‘yan jarida mai kula da sha’anin tsaro.

Sanarwar hukumomin tsaron ta kara da cewa ba wanda ya ji rauni a bangaren sojojin Nijar ballantana asarar rai , a cewar wani mai bin diddigin sha’anin tsaro a yankin Tafkin Chadi Kaka Touda Goni wannan alama ce dake nuna kwarewar dakarun Nijar a fannin yakin sunkuru.

Wasu majiyoyi sun ayyana cewa gagarumin farmakin da sojan saman Najeriya suka kaddamar a ‘yan kwanakin nan a yankin arewa maso gabashin kasar ne ya tilastwa ‘yan ta’addan kungiyar ISWAP gudowa Nijar da nufin samun mafaka a wani lokacin da ruwan Kogin Komadugu ya fara janyewa.

Sannan an yi katari matakan da Najeriya ta dauka na zuwa a wani lokacin da Jamhuriyar Nijar ta tsaurara matakan sama da kasa a yankin kudu maso gabashin kasar .

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG