Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Boko Haram Ta Hallaka Sojojin Najeriya Bayan Kammala Jana’izar Mutanen Da Hari Ya Rutsa Da Su


Fadan ya barke ne a ranar Talata lokacin da sojojin ke dawowa daga birne manoman da aka kashe kwanaki 2 da suka gabata a kauyen Dumba da ke gabar tafkin Chadi

Fafatawa tsakanin hukumomin tsaron Najeriya da mayakan boko haram ta hallaka sojoji 9 a arewa maso gabashin kasar, wasu dakarun soja 2 ne suka shaidawa afp hakan a yau Alhamis, kwanaki bayan da wata kungiyar ‘yan jihadin dake adawa da ita ta harbe gamman manoma.

Fadan ya barke ne a ranar Talata lokacin da sojojin ke dawowa daga birne manoman da aka kashe kwanaki 2 da suka gabata a kauyen Dumba da ke gabar tafkin Chadi, a cewar dakarun.

“Mun rasa 9 daga cikin sojojinmu a musayar wuta da ‘yan ta’addar Boko Haram sannan wasu 5 sun bata,” a cewar daya daga cikin dakarun.

An kuma jikkata soja guda, ya kara da cewa.

“Sojoji 7 sun mutu nan take yayin da 2 daga cikin wadanda suka jikkata suka cika a asibiti daga bisani,” kamar yadda soja na 2 ya shaidawa afp.

Sojojin na dawowa ne daga kauyen Tumbun Kanta inda suka taimakawa mazauna garin birne manoman da mayakan iswap suka hallaka a Lahadin data gabata a matsayin hukuncin yin kutse cikin yankinsu bada izini ba.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG