Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Babu Ranar Kawo Karshen Durkushewar Babban Layin Lantarki - Gwamnatin Najeriya


Wutar lantarki ta katse a duk fadin kasar Najeriya
Wutar lantarki ta katse a duk fadin kasar Najeriya

Ministan ya jaddada cewar yayin da ake sa ran matsalar durkushewar lantarkin ta ci gaba, gwamnati ta mayar da hankali wajen rage yawan faruwarsa tare da ba da tabbacin gyara shi a kan lokaci.

Babban layin lantarkin Najeriya zai ci gaba da fuskantar barazanar durkushewa saboda gazawar gwamnatin wajen gyara wani muhimmin layin wutar da ke shiyar arewacin kasar sakamakon matsalar rashin tsaron da ta ki ci ta ki cinyewa.

Wadannan sune kalaman Ministan Lantarki, Adebayo Adelabu, wanda ya bayyana hakan yayin zaman kare kasafin kudin ma’aikatarsa na bana a gaban kwamitin hadin gwiwar majalisar dattawan kasar a kan lantarki.

Adelabu ya yi tsokaci a kan illar lalata layin lantarkin na Shiroro-Kaduna-Mando, wanda ya daina aiki tun bayan lalata shi da aka yi a watan Oktoban 2024.

Wannan gazawar ta kara yin matsin lamba a kan babban layin lantarkin kasar, abin da ke sabbaba yawan durkushewarsa.

“Layin Kaduna-Shiroro-Mando yana daga cikin manyan layukan 2 da ke dakon lantarki zuwa arewacin Najeriya, na 2 shine, layin Ugwuaji-Makurdi, wanda shima an lalata shi sai dai an gyara. Amma layin Shiroro-Kaduna-Mando yana nan a lalace saboda rashin tsaro,” kamar yadda ya bayyana a jiya Litinin.

Ministan ya jaddada cewar yayin da ake sa ran matsalar durkushewar lantarkin ta ci gaba, gwamnati ta mayar da hankali wajen rage yawan faruwarsa tare da ba da tabbacin gyara shi a kan lokaci.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG