Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Za’a Dauke Wutar Lantarki Na Tsawon Makonni Biyu A Abuja


Ma'aikata na gyara a wasu turakun wutar lantarki a Najeriya (Hoto: X/TCN)
Ma'aikata na gyara a wasu turakun wutar lantarki a Najeriya (Hoto: X/TCN)

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Najeriya (TCN) ya ba da sanarwar zai dauke wutar lantarki a wasu sassa na babban birnin tarayya Abuja, daga ranar 6 ga watan Janairu zuwa 20 ga wata na wannan shekara.

Babbar Manajar sashen hulda da jama'a Misis Ndidi Mbah ce ta bayyana haka a wata sanarwa da ta sa hannu kuma ta raba wa manema labarai.

Mbah ta ce za a dauke wutar ne saboda aikin gyaran hanyoyin da hukumar raya babban birnin tarayya (FCDA) ta ke yi a yankin Unguwar Apo.

Mbah ta ce aikin zai shafi turakun wuta mai girman kilowat 132 da mai Kilowat 33 ta hanyar layin Kukwaba zuwa Apo, sannan kuma mai kilowat 132 ta babbar hanyar kudancin birnin taraiyya.

Mbah ta lissafa yankunan da abin ya shafa da suka hada da Kubwa, Karu, Maraba, Nyanya, Masaka, Keffi, Kukwaba, da kuma Unguwar Makanikai ta Apo.

Har ila yau, gyaran layin wutar zai kuma shafi sassan Unguwar Lugbe da Unguwar Trademore da Pyakasa, har zuwa Sabon Lugbe, Chika da Alaita.

Sanarwar ta kara da cewa “Wannan babban aiki ne na sake tsugunar da turken wutar lantarki da zai sa a dauke wutar daga ranar 6 zuwa 20 ga watan Janairu, daga karfe 9 na safe zuwa 4 na yamma a kowache rana.”

Kamfanin TCN ya ba da hakuri kan wannan tsawon lokaci da za’a dauke wuta a wadannan Unguwanni tare da fatan idan an gama gyaran za’a samar da wutar lantarki mai yawa zuwa tashar wuta ta Apo daga tashar wutar lantarki ta Gwagwalada, wanda zai sa unguwanin su samu wutar lantarki babu tsinkewa.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG