Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ana Fargabar Sabon Harin Anambra Ya Hallaka Mazauna Garin Nibo


Yan bindiga
Yan bindiga

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Tochukwu Ikenga, wanda ya tabbatar da harin yace al’amarin baya rasa nasaba da fadan kungiyoyin matsafan dake gaba da juna.

Al’ummar Nibo dake karamar hukumar Awka ta Kudu a jihar Anambra sun afka cikin rikici a jiya lahadi bayan da ake fargabar cewar ‘yan bindiga sun hallaka mutanen da ba’a san adadinsu ba a kusa da kasuwar Oye Nwochichi dake daura da asibitin karbar haihuwa na garin.

A cewar shaidun gani da ido, batagarin sun zo ne a cikin mota kirar jif “Lexus” mai launi ruwan kasa kuma ba tare da bata lokaci ba suka budewa mutane wuta.

Duk da cewar ba a kai ga tantance yawan mutanen da suka harbe din ba, al’ummar garin sun ce zuwa yanzu an gano akalla gawawwakin mutane 10.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Tochukwu Ikenga, wanda ya tabbatar da harin yace al’amarin baya rasa nasaba da fadan kungiyoyin matsafan dake gaba da juna.

Ikenga ya kara da cewar kwamishinan ‘yan sandan jihar, Nnaghe Itam, ya ba da umarnin tura karin jami’an ‘yan sanda zuwa yankin sannan ya bukaci mutanen da suka shaida afkuwar lamarin dasu taimaka da bayanai domin daukar matakin da ya dace.

“Rundunarmu na sane da abinda take zarki rikicin kungiyoyin matsafan da basa ga maciji da juna ne a yau 20/10/2024 a garin Nibo dake karamar hukumar Awka ta Kudu kuma kwamishinan ‘yan sanda, CP Nnaghe Obono Itam ya ba da umarni a gaggauta tura karin jami’an ‘yan sanda zuwa yankin domin daukar matakin da ya dace.

Dandalin Mu Tattauna

TASKAR VOA: Yadda Tsofaffi Ke Fama Da Lalular Yanar Ido A Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:26 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
TASKAR VOA: Fim Da Aka Shirya Kan Leah Sharibu Ya Samu Lambar Yabo
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:26 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

TASKAR VOA: Kalubalen Da Masu Fama Da Lalurar Galhanga Ke Fuskanta
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:26 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
TASKAR VOA: Tasirin Cibiyar Kula Da Lafiyar Mata Da Yara Ta HopeXchange A Ghana
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:41 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG