Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Ceto Mutane 5, Tare Da Gano Gawawwaki 9 Daga Hatsarin Kwale-Kwalen Zamfara


Hatsarin Jirgin Ruwan a Gummi
Hatsarin Jirgin Ruwan a Gummi

A cewar NEMA, kawo yanzu an gano gawawwakin fasinjoji 9, sannan ana cigaba da gudanar da aikin ceto.

An yi nasarar ceto mutane 5 tare da gano gawawwaki 9 daga hatsarin kwale-kwalen daya faru a lahadin data gabata a kogin Mashayar Yandaga dake karamar hukumar Gumin jihar Zamfara.

Sanarwar da kakakin hukumar bada agajin gaggawar Najeriya (NEMA), Manzo Ezekiel, ya fitar a yau Talata tace kwale-kwalen daya gamu da hatsarin na dauke ne da fiye da fasinjoji 40, galibinsu manoma da matukansa lokacin da ya kife sakamakon lodi fiye da kima da karfin igiyar ruwa.

An fidda sanarwar ne bayan da ofishin NEMA na Sokoto da takwaransa na Zamfara da hukumomin karamar hukumar Gumi da shugabannin al’umma da jami’an kungiyar bada agaji ta Red Cross da sauran masu ruwa da tsaki sun yi nazarin yadda iftila’in ya afku.

Bayan afkuwar hatsarin ne aka tattaro masu aikin ceto da suka kunshi gwanayen ninkayar yankin da masunta kuma suka yi nasarar ceto mutane 5 a raye.

A cewar NEMA, kawo yanzu an gano gawawwakin fasinjoji 9, sannan ana cigaba da gudanar da aikin ceto.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG