Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Zata Shirya Taron Jami'an Tsaron Kasashen Afirka


taron Sojojin AFRICOM
taron Sojojin AFRICOM

Ofishin jakadancin Amurka da ke Gaborone ya fitar da wata sanarwa inda ya ce Amurka za ta dauki nauyin shirya wani taro da zai tattaro manyan jami'an tsaro na kasashen Afirka a Botswana A mako mai zuwa

Masu gabatar da jawabai da mambobin kwamitin a taron zasu kunshi manyan jami’an farar hula da na soja, a cewar Laftanar Kanal Bobby Dixon, mai magana da yawun rundunar sojin Amurka a Afirka da ake kira AFRICOM.

ABUJA: AFRICOM
ABUJA: AFRICOM

Dixon ya ce, "Manufar taron ita ce tunkarar kalubalen tsaro a nahiyar Afirka da kuma gano hanyoyin aiki tare don samar da tsaro da kariya a Afirka. Kama daga kokarin yaki da ta'addanci zuwa barazanar kutsen yanar gizo da ayyukan wanzar da zaman lafiya, taron zai tattauna a kansu duka.

Rundunar AFRICOM ta ce taron zai dora kan nasarorin da aka samu a tarukan baya. Taron da aka yi a shekarar da ta wuce a birnin Rome na kasar Italiya, ya samu mahalarta mafi yawa, inda kasashe 43 suka tattaru.

Bayan taron kili kan harkokin tsaro da aka yi a watan Maris, Kungiyar Tarayyar Afrika ta bayyana matukar damuwa kan karin tashin hankali da ake fuskanta a nahiyar da kuma tasirin shi ga ci gaban nahiyar da zamantakewar al'umma.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG