Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Babban Limamin Masallacin Jos Ya Rasu


Sheikh Muhammad Lawal Adam
Sheikh Muhammad Lawal Adam

Wata sanarwa daga sakataren yada labarai na kungiyar JNI a jihar Filato, Sani Mudi, yace Sheihk Muhammad Lawal Adam ya rasu yana da shekaru tamanin a duniya.

Allah ya yi wa babban limamin masallacin Jos ta tsakiya Sheikh Muhammad Lawal Adam rasuwa a yammacin yau, Alhamis, 11 ga Yulin 2024, bayan gajeruwar rashin lafiya.

Wata sanarwa daga sakataren yada labarai na kungiyar JNI a jihar Filato, Sani Mudi, yace Sheihk Muhammad Lawal Adam ya rasu yana da shekaru tamanin a duniya.

Sanarwar tace malami ne kwararre, masanin shari'a na Musulunci, sanannen mai tafsiri na Alkur'ani mai girma kuma jagoran al'ummar Musulmi.

An nada shi mataimakin babban Limamin a shekara ta 2009 sannan kuma aka nada shi Babban Limamin a shekarar 2015.

Za a yi jana’izarsa gobe Jumma'a 12 ga Yulin da muke ciki da safe bayan sallar jana’iza.

Al"ummar Musulmin Jos sun yi matukar kewar wannan malami da ake girmamawa.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG