'Yan Bindiga Sun Kashe 'Ya'yan Wani Pasto A Jihar Adamawa
Yan bindiga
Rundunar yan sandar jihar Adamawa ta tabbatar da cewa ,
wasu 'yan bindiga sun kai hari gidan wani malamin addinin kirista suka kashe 'ya'yan malamin biyu su ka kuma arce da yar sa guda a yankin.
Njanrin gada dake karamar hukumar Hong.
Washington —
A hirar shi da Muryar Amurka, makwabcin limanin Kiristan Luka Yakubu ya bayyana cewa, ya dawo gida daga hira da misalin karfe goma na dare ne sai yaji ana ta harbi da bindiga a gidan Paston, da sai ya ji tsoro ya shiga daki don bashi da makamin da zai iya kare kansa ba. Bisa ga cewarsa, sun yi ta jira domin neman taimako daga jami'an tsaro amma har zuwa karfe biyu da wani abu basu samu agaji daga jami a tsaron yankin ba
A nasu bangaren, daya daga cikin jaurokan yankin Njanrin gada dake karamar hukumar Hong yayi ya bayyana yadda su ka sami gawawakin 'ya'yan Paston yayinda su ka tarar da Paston cikin jini shame shame. Nan take su ka yi kokarin kaisu asibiti anan aka tabbatar musu da mutuwa 'ya'yan.