Yadda Shugaban Hukumar Hisbah Ta Jihar Kano Ya Koma Kan Aikinsa

Your browser doesn’t support HTML5

Yadda Sheikh Aminu Daurawa Ya Dawo Kan Mukaminsa Na Shugaban Hukumar Hisbah

A yau Talata ne shugaban kwamandan Hisbah ta jihar Kano Mal Aminu Ibrahim Daurawa ya koma bakin aikinsa biyo bayan murubus da yayi a makon da ya gabata bayan wani jawabi da gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf yayi a gidan gwamnati yayin da yake ganawa da Malaman Addini.

KANO, NIGERIA - Jawabin dai na gwamna ya sa gwiwar kwamandan na Hisbah yayi sanyi kamar yadda ya fada a shafinsa na facebook a yayin da ya sanar da murabus dinsa daga shugabancin hukumar ta Hisbah.

Sheikh Daurawa (Hoto: Facebook/Hisbah)

Malamai da masu fada a ji ne na Arewacin Najeriya suka sanya baki domin tabbatar da cewa Malam Aminu Daurawa ya koma bakin aikinsa inda a daren jiya bayan ganawa da gwamna da kwamandan Hisbah ya bayyana dawowarsa kan aiki.

Ku Duba Wannan Ma Sheikh Aminu Daurawa Ya Dawo Kan Mukaminsa Na Kwamandan Hukumar Hisbah
Ku Duba Wannan Ma Shugaban Hukumar Hisbah, Sheikh Aminu Daurawa, Ya Yi Murabus

Ma’aikatan hukumar ta Hisbah da wasu jami’an gwamantin ne suka yi dafifi a ofishin na Hisbah domin tarbar kwamandan na Hisbah.

Taron Hisbah

Yayi jawabi ga manema labarai , inda ya bukaci matasa da yan Tiktok masu gurbata tarbiyya da su sauya hali tare da basu makwanni biyu domin gyara halayyarsu ko kuma su fuskanci fushin hukumar.

Saurari cikakken rahoto daga Mahmud Ibrahim Kwari:

Your browser doesn’t support HTML5

Yadda Shugaban Hukumar Hisbah Ta Jihar Kano Ya Koma Kan Aikinsa.mp3