Tsohon Gwamnan Lagos Lateef Jakande Ya Rasu

Alhaji Lateef Jakonde

Gwamnan farin kaya na farko a jihar Lagos, Lateef Jakande ya rasu yau Alhamis yana da shekaru 91 a duniya.

Lateef Jakande, wanda yake daya daga cikin almajiran tsohon firimiyan yankin kudu maso yammacin Najeriya, Obafemi Awolowo, ya yi mulki a matsayin gwamnan jihar Lagos tsakanin shekarar 1979 zuwa 1983.

Gwamnan jihar Lagos Babajide Sanwo-Olu ne ya sanar da rasuwar tsohon gwamnan Alhaji Lateef Kayode Jakande a shafinsa na Twitter

Gwamna Babajide Sanwo-Olu ya yaba aikin da marigayin ya yi lokacin yana dan jarida, da kuma shugabancin kwarai da marigayin ya yi a matsayin gwamnan jihar Lagos, da gwamnan ya ce zai zama abin koyi ga wadanda za su biyo baya. Ya bayyana rasuwar tsohon gwamnan a matsayin babban rashi ga jihar da kuma kasa baki daya.

Lateef Jakonde da Babajide Sanwo-Olu

Bayan gama wa’adin mulkinsa, marigayin ya kuma yi aiki a matsayin Ministan ayyuka karkashin mulkin soji na janar Sani Abacha. Yana daya daga cikin gwamnonin da ake yaba ayyukan raya jihohinsu a Najeriya, inda a zamanin sa, ya samar da ababan jin dadin rayuwa ga al’ummar jihar Lagos da suka hada da gidaje masu saukin kudi ga talakawa, da kuma yin gagarumin garambawul a fannin ilimi a duk fadin jihar, wanda kawo yanzu, babu gwamnan da ya doke wannan shirin.

Alhaji Lateef Jakande shi ne tsohon gwamnan jihar Lagos na biyu da suka rasu a cikin wannan shekarar. Kafin rasuwarsa, tsohon gwamnan jihar karkashin mulkin soja, Riya Admiral Ndubuisi Kanu ya rasu ranar 14 ga watan Janairu yana da shekaru 77 a duniya.