TSAKA MAI WUYA: Juyin Mulkin Nijar Da Takunkumin ECOWAS A Kasar, Kashi Na Shida - Satumba 12, 2023

  • Aliyu Mustapha

Aliyu Mustapha Sokoto

Shirin Tsaka Mai Wuya na wannan makon, zai kawo kashi na shida kuma na karshe na muhawara da ake kafsawa tsakanin Shu'aibu Mungadi da Zakari Jibrin kan abubuwan da suka biyo baya na juyin mulkin da aka yi a Jamhuriyar Nijar.

Shirin zai kuma duba tasirin wannan juyin mulkin a kan ita Nijar, Afirka da sauran kasashen duniya da kuma magana da wasu ke cewa shugaban ECOWAS kuma shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu bai san komai ba kan alaka tsakanin arewa ta Najeriya da Nijar.

Saurari shirin cikin sauti:

Your browser doesn’t support HTML5

TSAKA MAI WUYA: Juyin Mulkin Nijar Da Takunkumin ECOWAS A Kasar PT 6.mp3