Shugaba Tinubu Ya Koka Da Rasuwar Gwamna Rotimi Akeredolu

Bola Tinubu

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Shugaba Tinubu ya jajanta wa uwargidan Akeredolu, Betty, da kuma mukaddashin Gwamna Lucky Aiyedatiwa, inda ya bukace su da su samu karfin gwiwa a wannan jarrabawa ta babban rashi da ta sami kasa baki daya.

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya koka da Rasuwar Gwamnan jihar Ondo Rotimi Akeredolu.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Shugaba Tinubu ya jajanta wa uwargidan Akeredolu, Betty, da kuma mukaddashin Gwamna Lucky Aiyedatiwa, inda ya bukace su da su samu karfin gwiwa a wannan jarrabawa ta babban rashi da ta sami kasa baki daya.

A cikin karramawar da ya yi, Shugaba Tinubu, ya nuna matukar alhininsa game da rasuwar gwamnan jihar Ondo, Rotimi Akeredolu, inda ya bayyana shi a matsayin dan jiha mara tsoro kuma shugaba mai tausayi.

Shugaban ya bayyana Rotimi Akeredolu a matsayin fitacce kuma babban lauya, kuma tsohon shugaban kungiyar lauyoyin Najeriya, in da ya yaba da irin namijin kokarin da ya yi wajen tsara tsaran shari’a a kasa. Muhimmin rawar da ya taka wajen kafa rundunar tsaro a yankin Kudu maso Yamma ya nuna aniyarsa ta magance matsalolin tsaro.

Shugaban ya jaddada aikin da Akeredolu ya gada a tsawon shekaru shida da yayi yana gwamnan jihar Ondo. Tasirin Akeredolu ya bayyana a fili a cikin manyan ci gaban ababen more rayuwa, wuraren ilimi, da ayyukan kiwon lafiya da aka samar a fadin jihar.

Karramawar ta jaddada irin jagoranci na musamman da Gwamnan ya yi a lokuta da suke cike da jarrabawa da wahala, kamar abin da ya faru, inda aka kashe mabiya cocin Katolika 40 na Owo a shekarar 2022.

A karshe, Shugaba Tinubu ya yi kira ga Mukaddashin Gwamna Lucky Aiyedatiwa da ya tabbatar da ya cigaba da aiwatar da manufofin alheri na mulkin da tsohon shugaban ya bari.