Paparoma Francis Zai Isa Myanmar Yau

Myanmar Aung San Suu Kyi da Paparoma Francis

Paparoma Francis zai isa Myanmar yau Litinin, a wani yinkuri na jan hankalin duniya kan matsalar ‘yan gudun hijirar Rohingya.

Jagoran Majami’ar Katolikan zai wuce zuwa kasar Bangladesh ranar Alhamis.

Wuraren da Paparoman zai ziyarta ba su hada da sansanin ‘yan gudun hijira ba, to amma ana kyautata zaton zai gana da wasu ‘yan Rohingya a Dhaka, babban birnin kasar ta Bangaldesh.