Najeriya Ta Bi Sahun Sauran Kasashe Wajen Fara Azumi Ranar Litinin

Ramadan

An umarci ‘yan Najeriya da su tashi da azumin watan Ramadan ranar Litinin.

Mai alfarma sarkin Musulmi kuma shugaban hukumar koli ta harkokin addinin musulunci a Najeriya, Muhammad Sa’ad Abubakar, ya bayar da sanarwar ganin jinjirin watan azumin Ramadan na wannan shekara.

Sarkin Musulmi ya umarci al’ummar musulman Najeriya da su tashi da azumi ranar Litinin. Haka kuma ya yi kira ga dukkan ‘yan Najeriya da su tuna da shugabanni da kuma yadda yanayin kasar ke ciki musamman a sha’anin tsaro a dukkan ibadu da addu’o’i a tsawon wannan wata na Ramadan.

A wannan karon dai Najeriya ta yi muwafaka da kasar Saudiyya, wacce duk da yake ta fara duban wata tun ranar Asabar, amma ta bayar da sanarwar fara azumi ranar Litinin.

Saurari sanarwar mai alfarma Sarkin Musulman Najeriya.

Your browser doesn’t support HTML5

Najeriya: An Tashi Da Azumin Ramadan Ranar Litinin - 2'10"