Mun Wahala Matuka - Pep Guardiola

Mai horar da 'yan wasan Manchester City, Pep Guardiola (AP)

Guardiola ya bayyana hakan ne bayan da aka tashi a wasan kamar yadda kamfanin dillancin labarai na AP ya ruwaito.

Kocin Manchester City Pep Guardiola ya ce sun wahala sosai a wasan da suka kara da Real Madrid a zagaye na biyu na semi-final a gasar cin kofin zakarun nahiyar turai.

Guardiola ya bayyana hakan ne bayan da aka tashi a wasan kamar yadda kamfanin dillancin labarai na AP ya ruwaito.

“Wasan ya ba mu wahala, babu wanda zai musanta hakan.” In ji Guardiola.

Real Madrid ta doke Manchester City a zagaye na biyu a wasan semi-finals a gasar cin kofin ta Champions League a ranar Laraba

Hakan na nufin Real ce za ta hadu da Liverpool a wasan karshe na gasar ta UEFA.

An tashi a wasan ne da ci 3-1 inda dan wasan City Mahrez ya zura kwallon farko a minti na 73 a minti a ragar Real.

Sai dai Real ta yi kukan kura ta farke kwallon farko ta kuma kara wasu kwallaye biyu.

Dan wasan Madrid Rodrygo ne ya zura duka kwallayen biyun farko a minti na 90 da kuma 90+1.

Sai Kareem Benzema ya ci kwallo ta uku a bugun fenariti da Real ta samu.