Messi Ya Lashe Ballon d’Or

Lionel Messi (Photo by FRANCK F)

Wannan shi ne karo na takwas da Messi yake lashe wannan kambu inda ya doke Erling Haaland na Manchester City.

Lionel Messi ya lashe lambar yabo ta Ballon d’Or a karo na takwas a Paris, babban birnin Faransa.

Dan wasan na Argentina ya jagoranci kasarsa wajen lashe kofin duniya a Qatar a shekarar da ta gabata.

Kofin na gasar cin kofin duniya shi ne kadai da ya ragewa Messi ya lashe a rayuwarsa ta kwallo.

Messi wanda yake taka leda a kungiyar Inter Miami a Amurka ya doke Erling Haaland na Manchester City wajen lashe kyautar ta Ballon d’Or a bana.

‘Yar wasan Sifaniya Aitana Bonmati ce ta lashe kyautar ta Ballon d’Or a bangaren mata bayan da ta jagoranci kasarta ta lashe kofin gasar cin kofin duniya ta mata a watan Agusta.

Kazalika ta taimakawa Barcelona lashe kofin gasar zakarun nahiyar turai ta mata.