Hukumar MDD Tana Horas Da Matasan Najeriya Domin Su Dogara Da Kansu

Mataimakin Shugaban Kasa Yemi Osinbajo Ya Hallarci Taron

Shugaban asusun kula da yawan al'ummar Afrika na Majalisar Dinkin Duniya Mabingue Ngom, yace ya zama wajibi a kula da rayuwar yara mata ta hanyar basu ilimi mai inganci da tarbiyya, mutukar ana so a raya nahiyar Afrilka. Mr. Ngom yayi wannan kiran ne a wani taro da aka gudanar a ranar 11 ga wata Satumbar 2018 a Abuja.

Ya kuma nuna damuwa ga yadda ake nuna halin ko in kula ga rayuwar yara mata a nahiyar. Taken taron shine gudunmawar shuwagannin addinin musuluunci wajen karfafa hanyoyin dogaro da kai ta bangaren matasa maza da mata.

Sarkin Shanga, wanda ya wakilci Sarkin Musulmi Muhammad Sa'ad Abubakar a taron, ya bayyana yadda yawan matasa da magidanta marasa aikin yi yayi katutu a Najeriya, da kuma yadda hakan ke kawo wa kasar koma baya.

Ga Hauwa Umar da karin bayani...

Your browser doesn’t support HTML5

Bangaren Kula da yawan al'ummar Afrika na MDD Na Kokarin Koyawa Matasan Najeriya Dogaro Da Kai - 2'24