Haaland Ya Samu Sauki – Pep Guardiola

Haaland ya fita atisaye gabanin karawa da Young Boys

Haaland ya fita atisaye da sauran abokan wasansa na City gabanin karawar da kungiyar za ta yi da Young Boys a gasar Zakarun Turai a ranar Talata.

Manajan Manchester City Pep Guardiola, ya ce dan wasansa Erling Haaland ya samu sauki bayan da ya gurde kafarsa a karshen makon da ya gabata.

Haaland ya fita atisaye da sauran abokan wasansa na City gabanin karawar da kungiyar za ta yi da Young Boys a gasar Zakarun Turai a ranar Talata.

An dai cire Haaland a lokacin hutun rabin lokaci a karawar da City ta yi da Bournemouth wacce ta lallasa 6-1 a ranar Asabar bayan da ya gurde a kafa.

Guardiola ya ce an cire Haaland a wasan ne bayan da ya ce ba ya jin dadi.

“Na gana da likitan da shi kansa Haaland, ya ce min ya samu sauki.” Guardiola.