Gwamnatin Tarayya Najeriya tana taunawa a kaikaice da kungiyar Boko Haram

Shugaban kasar Najeriya Goodluck Jonathan

Najeriya tace ta fara tattaunawa da kungiyar Boko Haram da ake dorawa alhakin kashe daruruwan mutane

Najeriya tace ta fara tattaunawa da kungiyar Boko haram da ake dorawa alhakin kashe daruruwan mutane a hare haren boma bomai da harbe harben bindiga cikin watanni goma sha takwas da suka shige.

Majiyun siyasa da na diplomasiya da suka bukaci a saya sunayensu, sun ce masu shiga tsakani suna kai sakonni tsakanin kungiyar da gwamnati.

Rahotanni daga Najeriya na nuni da cewa, kungiyar Boko Haram ta bukaci a saki dukan membobinta da ake tsare da su a gidajen yari kafin ta daina kai hare hare. Gwamnati tana nazarin wannan tayin.

Shugaba Goodluck Jonathan yana fuskantar matsin lamba na neman dawo da zaman lafiya a arewacin kasar inda kungiyar Boko Haram take kai hare hare akasari kan jami’an ‘yan sanda da na gwamnati da kuma sauran hukumomi.

Aika Sharhinka