Gwamnatin Tarayya Na Kokarin Tsawaita Shirin Bada Tallafin Bankin Duniya

Bankin Duniya

A cewar wani kundin sauya fasalin aikin na Bankin Duniyan, gwamnatin Najeriya ta bukaci a tsawaita wa'adin kawo karshen aikin daga ranar 30 ga watan Yunin da muke ciki, zuwa 31 ga watan Disamban badi.

Najeriya ta bukaci tsawaita wa'adin shirin bada tallafin bankin duniya na rancen dala miliyan 800 da watanni 18 domin inganta shirye-shiryenta na baiwa al'umma kariya.

Bukatar na zuwa ne a daidai lokacin da kasar ke fama da matsalolin hauhawar farashi da kalubalen tattalin arziki.

A cewar wani kundin sauya fasalin aikin na Bankin Duniyan, gwamnatin Najeriya ta bukaci a tsawaita wa'adin kawo karshen aikin daga ranar 30 ga watan Yunin da muke ciki, zuwa 31 ga watan Disamban badi.

A cewar rahoton, kimanin magidanta masu karamin karfi milyan 3 suka ci gajiyar shirin tallafin rancen dala milyan 800.

Babban Bankin Najeriya ya rarraba rancen domin rage radadin manufofin gwamnati na baya-bayan nan, irinsu janye tallafin man fetur.

Daga cikin wadanda suka ci gajiyar shirin, magidanta dubu 700 sun fito ne daga yankunan karkara kuma kimanin magidanta milyan 2 da rabi sun fito ne daga birane.

Tsawaita wa'adin na neman a sake tsara wa'adin gudanar da aikin tare da inganta shirin gwamnatin najeriya na tallafawa al'umma, inda ya kara da cewar mazauna birni dubu 1 da 652 aka shigar cikin shirin ta hanyar tsarin zakulowa da shirin ya bullo da shi.