Gwamnatin Kano Ta Rushe Kwamitocin Rikon Kananan Hukumomi 44

Gwamna Abba Kabir Yusuf (Hoto: Facebook/Abba Kabir)

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya rushe kwamitocin rikon kananan hukumomin jihar 44.

An sanar da matakin, wanda ya fara aiki nan take ne, yayin wani taron bayyana yabo ga mambobin kwamitocin a dakin taro na ‘Africa House”, dake fadar gwamnatin kano.

Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, ta bayyana cewa “rushe kwamitoci ya kawo karshen wa’adinsu na watanni 6, sa’ilin da suka yi aiki kafada da kafada da gwamnatin jihar wajen aiwatar da manufofi da tsare-tsarenta ga al’umma na kasa.

Gwamnan ya umarci cewa a mika al’amuran gudanar da kananan hukumomin hannun daraktocin gudanarwa (DPM) na kowace daga cikinsu har sai an kammala zabubbukan kananan hukumomin da zasu gudana a ranar 26 ga watan Oktoba mai kamawa.