Ghana Ta Ce Bata Bada Umarnin Fitar Da Sanarwa Cewa 'Yan Kasar Su Yi Taka Tsantsan Da Tafiya Abuja Ba

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da na kasar Ghana Nana Akufor Addo a wajen Taron ECOWAS na 52

Gwamnatin Ghana ta ce ba da izinin ta ma’aikatar harkokin wajenta ta fitar da sanarwa jiya Laraba cewa ‘yan kasar su yi hattara saboda akwai yiwuwar kai hare-haren ta’addanci a birnin Abuja ba.

A wata sanarwa ta daban, ma’aikatar ta ce bata da wata masaniya akan auna wani dan Ghana a birnin Abuja.

Sanarwar ta ce “Bamu da labarin wata barazana dake auna ‘yan Ghana wadanda ke ci gaba da zaman lafiya da ‘yan uwansu ‘yan Najeriya maza da mata.”

Ghana Government Statement

A don haka ma’aikatar harkokin wajen ta yi nadama kana ta roki gafara akan duk wata damuwa da wannan sanarwar ta haifar. Ta kuma ce a yi watsi da wannan sanarwa kwata-kwata.

A watan da ya gabata, Amurka, Birtaniya da wasu kasashen ketare suka fitar da sanarwa, inda suka yi kira ga ‘yan kasarsu da su yi hattara saboda akwai yiwuwar kai hare-haren ta’addanci a birnin na Abuja.

Hukumomin Najeriya sun yi watsi da sanarwar ta Amurka da Birtaniya kan yiwuwar kai hare-hare a Abuja inda suka ce babu wani abu makamancin haka.

A sanarwar ta jiya Laraba da Ghana take nisanta kanta da ita, ta ce ta dauki wannan mataki ne lura da umarni da hukumomin Najeriya suka ba wasu otel-otel na su rufe harkokinsu. Sanarwar ta kuma ce, “Idan har ya zama dole sai an yi tafiya zuwa birnin na Abuja, akwai bukatar a yi takatsantsan."