An Soke Tafiyar Shettima Zuwa Samao Saboda Lalacewar Jirgi A New York  

Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima (Hoto: Facebook/Kashim Shettima)

Tuni dai Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima da Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Yusuf Tuggar, suka baro New York zuwa Najeriya.

An soke tafiyar Mataimakin Shugaban Najeriya Kashim Shettima domin wakiltar kasar a taron shugabannin kasashen kungiyar kasashe renon Ingila (Commonwealth), bayan da wani abu ya daki jirginsa a filin saukar jiragen saman JFK dake birnin New York.

Sanarwar da mashawarcin shugaban Najeriya akan harkokin yada labarai da tsare-tsare, Bayo Onanuga ya fitar, tace abinda ya daki jirgin ya fasa gilashin gaban direban jirgin.

Shugaba Tinubu ya amince tawagar ministoci ta wakilci Najeriya a taron da zai gudana a Apia, babban birnin Samao, yayin da aka fara aikin gyaran jirgin.

Tawagar, da a yanzu za ta wakilci Najeriya a taron za ta kasance karkashin jagorancin Ministan Muhalli, Balarabe Abbas Lawal.

An samo taron wanda yanzu haka ke gudana a kasar dake tsibirin yankin pacific a rana 21 ga Oktoban da muke ciki, kuma za a kammala shi a gobe 26 ga watan.

Tuni dai Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima da Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Yusuf Tuggar, suka baro New York zuwa Najeriya.