Akwai Yiwuwar Mu Gana Da Shugaban Iran Hassan Rouhani -Trump

Shugaba Trump (Hagu) da shugaba Macron (Dama)

Shugaban Amurka Donald Trump, jiya Litinin, ya ce, “akwai matukar yiwuwar ya gana da Shugaban Iran, Hassan Rouhani, cikin ‘yan makonni masu zuwa, don a sake tattaunawa kan wata sabuwar yarjajjeniya ta kawo karshen shirin nukiliyar Iran.

Sabuwar yarjajeniyar za ta maye gurbin ta kasa da kasa ta 2015, wacce Trump ya janye daga cikinta a bara.

Trump, wanda ke magana bayan taron G7 na shugabannin manyan kasashen duniya a Faransa, ya ce, “ina ganin Iran za ta zo ta bukaci a gana.”

Shugaban na Amurka ya ce takunkumin tattalin arzikin da ya sake kakaba wa Iran shekara guda da ta gabata ya na, a cewarsa, “addabarsu matuka,”ganin yadda shi Trump din ya yi matukar takaita hanyoyin sayar da man Iran a kasuwannin duniya.

Da ma shugaban Faransa, Emmanuel Macron, ya sha kokarin shirya tattaunawar zaman lafiya tsakanin Amurka da Iran.

Macron ya gaya ma wani taron manema labarai a gaban Trump cewa ya tattauna da shugaba Rouhani kuma, inji shi, shugaban na Iran na da niyyar ganawa da Trump.