Wakilin AU PM Ra'ila Odinga, Ya Katse Shawarwari Da Yake Yi A Cote D'Voire

Shugaban Ivory Coast laurent Gbagbo daga hagu yake magana da PM Kenya Ra'ila Odinga.

Jiya Talata,Matakan diplomasiyyar da ake dauka domin kawo karshen rikicin siyasar dake addabar kasar Ivory Coast ya hadu da cikas

Jiya Talata,Matakan diplomasiyyar da ake dauka domin kawo karshen rikicin siyasar dake addabar kasar Ivory Coast ya hadu da cikas, domin Friministan kasar Kenya Raila Odinga, wakilin kungiyar hadin kan kasashen Afirka mai shiga tsakanin ya katse tattaunawar da yake yi ba shiri ya koma gida a safiyar yau Laraba.

Duk da haka Odinga yace ya sami ci gaba na azo a gani, domin akwai alamar dake nuna cewa sassan biyu zasu iya haduwa domin tattaunawa fuska da fuska idan har za’a cimma wasu sharudda.