Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

'Yan Kabilar Rohingya Masu Gudun Hijira Sun Zargi Jami'an Tsaron Gwamnati


‘Yan gudun hijirar Rohingya dake Bangladesh sun zargi jami’an tsaron gwamnatin Myanmar da laifin keta hakkin bil’adama dayawa biyo bayan hare-haren da ‘yan bindigar kungiyar Arakan Rohingya Salvation Army suka kai ranar 25 ga watan Agustan wannan shekarar.

A ranar 25, ga watan agusta da ya gabata ne aka kai hari akan ofisoshin ‘yan sanda da sansanonin sojoji a jihar Rakhine dake arewacin kasar, amma ba a bayyanawa ‘yan jarida da ‘yan rajin kare hakkokin bil’adama irin wadannan munanan abubuwan ba. Yara ne suka zana su.

Anthony Lake, shugaban hukumar tallafawa yara kanana ta majalisar dinkin duniya da ake kira UNICEF, ya fadawa manema labarai a Cox jiya Talata cewa, “a lokacin da suke aiki da yaran da suke kokarin taimakawa don su warware daga dimuwar da suka sami kansu ciki, daya daga cikin abin da suke yi shine sa yaran su zana hotuna.

Mr. Lake yace ya gani a wurare da yawa hotunan zanen dake nuna farin ciki daga yara, a wasu wuraren kuma, hotunan da muke gani sun sha bambam.

Hotunan da muke gani a nan munana ne. suna nuna irin abubuwan da bai kamata yaro ya gani ba, balle ma ya fuskancesu, a cewar Lake.

A wani hoton, wasu mutane da yaran suka zana a matsayin sojoji sun harbe fararen hula yayinda wasu kuma da tayiwu bata gari ne, suka yi amfani da takkubba suka caccaki wasu mutane da basa dauke da wani makami.

Facebook Forum

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG