Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaba Bola Ahmed Tinubu Ya Gana Da Gwamnonin Jihohin Iyakar Nijar


Tinubu ya gana da gwamnonin iyakar Nijar
Tinubu ya gana da gwamnonin iyakar Nijar

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi wata muhimmiyar ganawa da gwamnonin jihohin Najeriya dake da iyaka da kasar Jamhuriyar Nijar.

An gudanar da ganawa ta musamman din ne a yammacin Lahadi, 6 ga Agustan 2023 a fadar gwamnati da ke Abuja, inda Shugaba Tinubu ya gana da gwamnonin jihohin Najeriya da ke kan iyaka da Jamhuriyar Nijar.

Ganawar shugaban da gwamnonin wani bangare na tuntubar da shugaban kasar ke yi dangane da lamarin da ke faruwa a kasar Nijar na juyin mulki da sojoji suka yi a ‘yan kwanakin nan da kuma matakan kungiyar ECOWAS da shugaban Najeriya ke jagoranta.

Taron ya samu halartar manyan gwamnonin da suka hada da Gwamna Ahmed Aliyu na Sokoto, Umar Namadi na Jigawa, Mai Malam Buni na Yobe, Idris Nasir na Kebbi, da Gwamna Dr Dikko Radda na Katsina.

~ Yusuf Aminu Yusuf

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG