Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shekarar Farko Na Mulkin Tinubu: Mun Kubatar Da Duk Yaran Da Aka Yi Garkuwa Da Su - Babban Hafsan Tsaro


Babban Hafsan Tsaron Najeriya Janar Christopher Gabwin Musa
Babban Hafsan Tsaron Najeriya Janar Christopher Gabwin Musa

Hafsan Hafsoshin Sojin Najeriya Janar Christopher Musa ya bayyana cewa, al’ummar kasar na da gagarumar gudummuwar da za su iya badawa a yunkurin shawo kan matsalar tsaro da ake fuskanta a kasar.

Janar Christopher Musa ya tabattar da hakan ne yayin wata hira ta musamman da Shugaban Sashen Hausa na Muryar Amurka, Aliyu Mustapha, a Abuja, birnin tarayyar Najeriya, inda ya zayyana matakan da su ke dauka na shawo kan wannan matsalar.

Bisa ga cewar sa, taimako daga Allah da kuma hadin kan da su ke samu daga jama’a sun taimaka gaya. Ya kuma bayyana cewa, ya kamata mutane su sani cewa akwai miyagun mutane a tsakanin al'umma da ke karban kudin jini, kuma tilas ne a yi masu iyaka idan ana son ganin bayan ayyukan su.

Ya kuma nuna bakin cikinsa ganin yadda lamarin ya fi shafar arewacin Najeriya.

Ya kara da cewa cikin shekara dayan da aka cika karkashin mulkin shugaba Tinubu, an samu nasarar samun kwanciyar hankali a wuraren da ake fuskantar matsolin tsaro, yayinda aka kuma samu nasarar kubutar da yaran da aka yi garkuwa da su a sassa daban daban na kasar.

Janar Christopher MusaYana yace, fatansu shi ne su ga manoma sun koma noma kuma jama'a sun koma gidanje su ko kuma kasuwanci cikin kwanciyar hankali.

Saurari wannan bangaren hirar:

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:36 0:00

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG