Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

QATAR 2022: Samuel Eto’o Ya Yi Nadama Game Da Hatsaniya A Wajen Gasar Cin Kofin Duniya


Shugaban hukumar kwallon kafar Kamaru kuma tsohon dan wasan kwallon kafa Samuel Eto’o
Shugaban hukumar kwallon kafar Kamaru kuma tsohon dan wasan kwallon kafa Samuel Eto’o

Shugaban hukumar kwallon kafar Kamaru kuma tsohon dan wasan kwallon kafa Samuel Eto’o ya nemi afuwar wani mutum da ya ture kasa a wani abin da ya kira ‘mummunar hatsaniya’ a wajen wani filin wasa na gasar cin kofin duniya da safiyar Talata.

Eto'o ya dan dakata ne don daukar hotuna tare da magoya bayansa a kusa da filin wasa na 974 bayan Brazil ta doke Koriya ta Kudu da ci 4-1. Hotunan da ke yawo a shafukan sada zumunta sun nuna shi yana mayar da martani kan kalaman wani mutum rike da kyamara.

Eto'o ya rubuta a cikin kalaman da aka wallafa cikin harshen Faransanci da Ingilishi a shafinsa na Twitter, inda ya ce "Na yi mummunan rikici da wani wanda watakila mai goyon bayan Aljeriya ne ,"

Eto'o, wanda ya wakilci kwamitin shirya gasar cin kofin duniya ta Qatar a matsayin jakadan Global Legacy tun daga shekarar 2019, ya ce "Ina so in nemi afuwar rashin hakuri da na nuna, da rashin jin dadi da kuma mayar da martani ta hanyar da bai dace da halina ba."

Mutumin mai suna Said Mamouni dan kasar Algeria, daga baya ya buga wani faifan bidiyo a YouTube yana mai cewa shi ne wanda aka kai wa naushi, kuma yana ofishin ‘yan sandan Qatar domin ya shigar da kara a kan Eto’o.

Ya ce Eto’o ya shiga tashin hankali ne bayan da Mamouni ya tambaye shi ko ya bai wa alkalin wasa Bakary Gassama cin hanci a wasan da Kamaru da Aljeriya suka fafata a gasar neman shiga gasar cin kofin duniya.

Kamaru ta samu nasara a karawa ta biyu da ci 2-1 a wasan karshe na wasan inda ta samu tikitin shiga gasar cin kofin duniya bisa ka’idar cin kwallaye a waje.

Hukumar kwallon kafar Aljeriya ta shigar da kara ga hukumar kwallon kafa ta FIFA, inda ta bukaci a sake buga wasan saboda wasu kura-kurai da Gassama ya yi. FIFA ta yi watsi da korafin.

Sai dai kuma korafin Aljeriya ya kai ga taron manema labarai na tawagar Kamaru a Qatar, kwana daya kafin su kara da Switzerland. Tambayar da wani dan jarida dan kasar Algeria ya yi wa kocin Kamaru Rigobert Song game da "ko sun sayi tikitin shiga gasar ne" amma ba a amsa ba.

FIFA ba ta amsa bukatar yin sharhi nan take ba. Mai magana da yawun hukumar ta Kamaru bai amsa kiran waya nan take ba bai kuma amsa sakonnin neman sharhi ba.

Gwamnatin Qatar ma ba ta amsa tambayoyi kan lamarin ba nan take.

XS
SM
MD
LG