Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Najeriya ta Kulla Yarjejeniya da Faransa


Shugaban kasar Faransa Francois Hollande da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari
Shugaban kasar Faransa Francois Hollande da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya sa hannu a wata sabuwar yarjejeniya da kasar Faransa a fannonin aikin soja, da ayyukan noma da kuma wutar lantarki.

Shugaban Najeriya da takwaransa na kasar Faransa Francois Holland sun sa hannu a yarjejeniyar ne yau, kafin bude taron koli kan harkokin tsaro dake kankama a birnin tarayya Abuja.

Kasar Faransa ta amince zata taimakawa Najeriya ta fannin horas da jami’an tsaro da samar da bayanan leken asiri ,da kuma wadansu dabaru yaki, a yunkurin kakkabe mayakan kungiyar Boko Haram.

Har wa yau, kasar Faransa zata tallafa a fannin ayyukan noma da nufin rage dogaro ga albarkatun man fetir da Najeriya ke yi, ganin yadda ake ci gaba da samun faduwar farashin danyen mai a kasuwannin duniya.

Faransa zata kuma taimaka a fannin ayyukan wutar lantarki da ake kyautata zaton zai taimaka gaya wajen farfado da masana’atun kasar da suka durkushe da kuma samar da ayyukan yi musamman tsakanin matasa.

Ga rahoton da wakilinmu Umar Faruk Musa ya aiki daga Abuja, Najeriya.

Najeriya ta kulla yarjejeniya da Faransa-2:12"
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:17 0:00
Shiga Kai Tsaye

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG