Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Manyan Jami’an Kungiyar EU Da Shugaban Afrika ta Kudu Za Su Yi Wani Babban Taro


Shugaban majalisar tarayyar Turai Antonio Costa da Shugaban kasar Afrika ta Kudu Cyril Ramaphosa da Shugabar hukumar tarayyar Turai Ursula von der Leyen a babban taron EU a Tuynhuys na Cape Town
Shugaban majalisar tarayyar Turai Antonio Costa da Shugaban kasar Afrika ta Kudu Cyril Ramaphosa da Shugabar hukumar tarayyar Turai Ursula von der Leyen a babban taron EU a Tuynhuys na Cape Town

A ranar Alhamis manyan jami'an kungiyar Tarayyar EU suka tattaru a Afirka ta Kudu don halartar wani taron koli da Shugaban kasar Cyril Ramaphosa, taron da zai maida hankali kan karfafa huldar kasuwanci da diflomasiyya yayin da dukkan kasashen ke jin tasirin manufofin harkokin waje na gwamnatin Trump

Shugabar hukumar tarayyar Turai Ursula Von der Leyen da Shugaban Majalisar tarayyar Turai António Costa, za su gana da Ramaphosa a ofishinsa da ke Cape Town a taron EU da Afirka ta Kudu na farko da za su yi tun shekarar 2018.

EU Africa Summit
EU Africa Summit

Kungiyar kasashen mai mambobi 27 za ta karkatar da hankalinta ne kan babbar kasar da take huldar kasuwanci da ita a yankin kudu da hamadar Sahara, bayan da kungiyar EU ta sanar da kakaba haraji kan Washington a matsayin martani kan sabon harajin da shugaban Amurka Donald Trump ya sanya kan karahuna da dalma da kasashen ke kaiwa Amurka.

Taron da za a yi a Afirka ta Kudu zai "duba sabbin hanyoyin hadin gwiwa a fannin tattalin arziki, kasuwanci da zuba jari, da kuma tattauna duk wani kalubale ko takaddamar cinikayya da ke tsakanin kasashen," in ji majalisar zartarwa EU.

Ursula von der Leyen ta gaida Shugaban kaşar Afrika ta Kudu Cyril Ramaphosa
Ursula von der Leyen ta gaida Shugaban kaşar Afrika ta Kudu Cyril Ramaphosa

Gwamnatin Trump dai ta sanya wa Afrika ta kudu takunkumi saboda wasu manufofin cikin gida da na waje da shugaban na Amurka ya bayyana a matsayin wadanda basu je daidai da muradan Amurka ba.

A watan da ya gabata ne Trump ya ba da umarnin dakatar da duk wasu kudade da Amurka ke ba Afirka ta kudu, inda ya zargi kasar da take hakkokin bil'adama akan farar fata tsiraru a kasar, da kuma goyon bayan wasu "miyagu" a duniya, kamar kungiyar gwagwarmayar Palasdinawa ta Hamas da kuma Iran.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG