Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Majalisar Dinkin Duniya Ta Yi Tir Da Kashe-Kashen Borno


Malick ya jajantawa iyalan mutanen aka hallakan tare da yiwa wadanda suka jikkata fatan samun lafiya cikin hanzari sannan yace Majalisar Dinkin Duniyar na tare da gwamnati da al’ummar jihar Borno.

Majalisar Dinkin Duniya ta yi allawadai da kisan kiyashin da aka yiwa farar hula na baya-bayan nan a yankin kukawa na jihar Borno, dake shiyar arewa maso gabashin Najeriya.

Sanarwar da jami’in ayyukan jin kai na majalisar a Najeriya, Muhammad Malick, ya fitar ta bayyana kisan gillar da aka bada rahoton cewar mambobin wata kungiya mai dauke da makamai ta yiwa akalla fafaren hula 40 a kauyen Dumba a ranar 12 ga watan Janairun da muke ciki, da abin tsaro da tada hankali.

An ba da rahoton cewa an hallaka mutanen da galibinsu manoma da masunta ne bayan da ake zarkin sun sabawa haramcin da kungiyar ‘yan bindigar ta sanya a kan ayyukan da suka shafi noma.

Malick ya jajantawa iyalan mutanen aka hallakan tare da yiwa wadanda suka jikkata fatan samun lafiya cikin hanzari sannan yace Majalisar Dinkin Duniyar na tare da gwamnati da al’ummar jihar Borno.

Ya kuma bukaci a gano wadanda suka aikata kisan tare da gurfanar dasu gaban shari’a.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG