Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Macron  Ya Fusata Da Harin Da Isra'ila Ta Kai A Rafah


Shugaban Faransa Emmanuel Macron
Shugaban Faransa Emmanuel Macron

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bayyana bacin ransa a yau Litinin kan harin da Isra’ila ta kai kan sansanin Falasdinawa da suka rasa matsugunansu a Rafah, wanda jami’an Gaza suka ce sun kashe akalla mutane 45,  tare da neman a tsagaita bude wuta nan take.

"Dole ne a dakatar da wadannan ayyukan. Babu wani wuri da fararen hula Faladinawa su ke zaune cikin kwanicyar hankali a Rafah," in ji Macron a kan shafin X.

"Ina kira da a mutunta dokokin kasa da kasa da kuma tsagaita bude wuta nan take."

Sansanin da Isra'ila ta kona a Rafah
Sansanin da Isra'ila ta kona a Rafah

Ma'aikatar lafiya a Gaza ta Hamas ta ce adadin wadanda suka mutu ya karu zuwa 45 daga hare-haren da Isra'ila ta kai cikin dare, wanda ya haddasa gobara da ta kashe mutanen da suka rasa matsugunansu a cikin tantunansu, wadanda yawancinsu mata da yara ne.

Rundunar sojin Isra'ila ta ce tana gudanar da bincike kan rahotannin fararen hula da aka kashe a hare-haren, wanda ya janyo tofin Allah tsine a kasashen Larabawa.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG