Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Macron  Ya Fusata Da Harin Da Isra'ila Ta Kai A Rafah


Shugaban Faransa Emmanuel Macron
Shugaban Faransa Emmanuel Macron

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bayyana bacin ransa a yau Litinin kan harin da Isra’ila ta kai kan sansanin Falasdinawa da suka rasa matsugunansu a Rafah, wanda jami’an Gaza suka ce sun kashe akalla mutane 45,  tare da neman a tsagaita bude wuta nan take.

"Dole ne a dakatar da wadannan ayyukan. Babu wani wuri da fararen hula Faladinawa su ke zaune cikin kwanicyar hankali a Rafah," in ji Macron a kan shafin X.

"Ina kira da a mutunta dokokin kasa da kasa da kuma tsagaita bude wuta nan take."

Sansanin da Isra'ila ta kona a Rafah
Sansanin da Isra'ila ta kona a Rafah

Ma'aikatar lafiya a Gaza ta Hamas ta ce adadin wadanda suka mutu ya karu zuwa 45 daga hare-haren da Isra'ila ta kai cikin dare, wanda ya haddasa gobara da ta kashe mutanen da suka rasa matsugunansu a cikin tantunansu, wadanda yawancinsu mata da yara ne.

Rundunar sojin Isra'ila ta ce tana gudanar da bincike kan rahotannin fararen hula da aka kashe a hare-haren, wanda ya janyo tofin Allah tsine a kasashen Larabawa.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG